Bakonmu A Yau
Tattaunawa da Dakta Nasiru Sani Gwarzo kan giɓin kasafin da WHO ke fuskanta
- Author: Vários
- Narrator: Vários
- Publisher: Podcast
- Duration: 0:03:40
- More information
Informações:
Synopsis
Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta fara babban taronta karo na 79 jiya Litinin a birnin Geneva, wanda kuma za a ƙarƙare shi a ranar 23 ga watan Mayu da muke. Daga cikin muhimman batututwan da taron zai fi mayar da hankali a kai dai akwai giɓin kasafin kuɗin da ya kai Dala Biliyan 1 da Hukumar Lafiyar ta Duniya ke fuskanta, da kuma tasirin janyewa daga cikinta da Amurka ta yi. Kan wannan da kuma sauran batutuwa masu alaƙa, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Nasiru Sani Gwarzo, ƙwrarre kan sha’anin lafiya da ke Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.